Rahotanni daga Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya na cewa, wani 'dan kunar bakin wake ya halaka wasu mutane 2, kana wasu mutane hudu kuma suka jikkata bayan da ya tayar da bam din da ya dana a cikin mota da ya ke ciki.
Kwamishinan lardin Bondhere Qasim Abdullahi, ya shaidawa manema labarai a wurin da lamarin ya faru a yammacin jiya Lahadi cewa, maharin ya tayar da bam din da ke cikin motar tasa ce a wajen wani wurin cin abinci da ke kusa da wurin tarihi na Daljirka Dahsoon a lardin na Bondhere.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, fashewar tana da karfin gaske, kuma ta sanya mutane ranta cikin na kare.
Sai dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kaddamar harin, amma kuma kungiyar Al-Shabaab tana kaddamar da hare-hare a kai a kai a cikin kasar, galibi a Mogadishu, babban birnin kasar.(Ibrahim)