in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da kazamin hari a Somaliya
2016-09-01 09:22:26 cri

Wakilin musamman na MDD a kasar Somaliya, Michael Keating, ya yi kakkausar suka game da mummunan harin da aka kaddamar a otel din SYL a Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya, wanda ya hallaka mutane a kalla 13, sannan ya jikkata mutane 20.

Mai magana da yawun MDD Stephane Dujarric, ya shedawa 'yan jaridu ajiya Laraba cewa, Keating ya bayyana harin na otel din SYL a matsayin kwakkwarar hujja game da irin barnar da ake yiwa al'ummar Somaliya wadanda suke adawa da hare haren ta'addancin kungiyar al-Shabaab.

Dujarric ya ce, harin shi ne karo na 3 da ake kaddamarwa kan otel din SYL daga farkon shekarar 2015.

Bugu da kari Keating ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China