in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan sanda a Burkina Faso sun kashe wani da ake zargi mai jihadi ne
2016-10-24 09:18:53 cri

Kwamishinan 'yan sanda na kasar Burkina Faso Lazare Tarpaga ya ce, jami'ansa sun yi nasarar kashe wani da ake zaton mai kishin jihadi ne, yayin wani samame da suka kaddamar a cibiyarsu da ke yankin arewa maso yammacin wajen birnin Ouagadougou, babban birnin kasar da nufin tarwatsu.

A cikin wata sanarwa da 'yan sandan suka rabawa manema labarai, sun bayyana cewa, mutumin yana rike da wata karamar bindiga da kuma wani abin fashewa a lokacin da suka harbe shi a musayar wutar da suka yi.

Hukumomin tsaro sun bayyana cewa, 'yan sandan sun kuma yi nasarar kama wasu daga cikin masu ra'ayin jihadin, sai dai kuma ba a bayyana adadin mutanen da aka kama ba. Yanzu haka dai ana ci gaba da gudanar da bincike.

A cewar kwamishinan 'yan sandan, 'yan ta'addan suna kokarin daukar matasa ne domin su shigar da su kungiyarsu.

A 'yan shekarun da suka gabata dai kasar Burkina Faso tana fama da hare-haren ta'addanci da yunkurin juyin mulki daga rukunin sojoji na musamnan da ke gadin fadar tsohon shugaban kasar Blaise Compaore. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China