in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisun dokokin Burundi sun kada kuri'ar ficewar kasar daga kotun ICC
2016-10-13 10:04:12 cri

A jiya Larabe ne majalisun dokokin kasar Burundi suka kada kuri'ar ficewa daga kotun hukunta manyan laifuffuka ta duniya(ICC)

Ministan shari'a na kasar Burundi Aimee Laurentine Kanyana wanda ya halarci zaman kada kuri'ar ficewar, ya ce, kasar Burundi ta fice daga kotun ne, saboda ba abin da kotun ta ke yi, illa yaki da kasashen Afirka.

Yayin da jam'iyyar CNDD-FDD mai mulki ta ke kallon matakin ficewa daga kotun a matsayin wanda ya dace, su kuma 'yan majalisun da ke adawa da gwamnati, sukar lamarin suka yi, suna masu cewa, mataki ne da ba za a hukunta masu aikata manyan laifuffuka ba.

A makon da ya gabata ne, mataimakin shugaban kasa na daya Gaston Sindimwo ya sanar da cewa, Burundin ta yanke shawarar ficewa daga kotun hukunta manyan laifuffuka ta kasa da kasa (ICC) saboda 'yan Afirka kawai ta ke hukuntawa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China