Firaminista da gwamnatinsa za su ci gaba da tsaya wa kan aiki,kuma gwamnatin ba za ta yi murabus ba, in ji kakakin gwamnatin Libiya, Hatem Oaribi, tare da cewa gwamnati ta tsaya a shirye domin bayyana a gaban majalisar dokoki inda za ta sake jaddada nauyin da ke wuyanta a kowa ne lokaci.
A ranar Laraba, mista Theni ya sanar a yayin wata hira da wani gidan talabijin mai zaman kansa na kasar Jordan cewa zai sauka daga mukaminsa, bayan an soki fadarsa da kasa tabuka kome wajen warware matsalolin Libiya. (Maman Ada)