Najeriya ta kasa cimma burinta na samar da man fetur na kasafin kudin kasa na shekarar 2016, na kimanin gangar dayen mai miliyan 2,2 a ko wace rana, in ji ministan kasafin kudi da fasalin kasa a ranar Talata. Minista Udoma Udo Udoma, ya bayyana hakan a yayin wani dandalin shekara shekara na kamfanin tattalin arzikin Najeriya (NES) karo na 57, cewa, kasar ta samu cimma kawai samar da gangar danyen mai miliyan 1,1 a kowace rana a cikin watan Augusta. Kwamitin kula da tattalin arziki na cikin aikin bullo da wasu jerin matakan ba da kuzari, ta yadda za a ingiza tattalin arziki dake cikin matsala. (Maman Ada)