in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya gana da shugaban Afirka ta Kudu game da zaman lafiya da tsaro
2016-09-19 10:07:18 cri

Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya zanta da shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma a birnin New York na kasar Amurka, game da harkokin wanzar da zaman lafiya, da sauyin yanayi da tsaro a nahiyar Afirka.

Da yake karin haske game da hakan, kakakin MDDr Stephane Dujarric, ya ce, yayin zantawar ta su, Ban Ki-moon ya jinjinawa Afirka ta Kudu bisa namijin kokari da take yi, wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a nahiyar.

Kaza lika ya yi kira ga mahukuntan kasar da su rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi cikin hanzari, tare kuma da mai da hankali ga batutuwan 'yan ci rani, da masu gudun hijira, cikin hadin gwiwa da sauran kasashen duniya.

A daya bangaren kuma jami'an biyu, sun jaddada muhimmancin hawa teburin shawara game da yanayin da ake ciki a kasashen Sudan ta Kudu, da Burundi da janhuriyar dimokaradiyyar Congo.

Shugaba Zuma dai ya isa birnin New York ne domin halartar babban taron MDD, wanda za a bude a gobe Talata a helkwatar majalissar.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China