in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Zuma ya taya tawagar kasarsa murnar samun nasara a gasar Olympic ta Rio
2016-08-22 10:26:14 cri

Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma, ya taya tawagar kasar sa da ta halarci gasar Olympic ta birnin Rio murnar samun lambobin yabo a gasar ta bana.

Afirka ta kudu dai ta lashe lambobin yabo 10, da suka hada da lambobin zinari biyu, da azurfa 6 da kuma tagulla biyu.

Shugaba zuma ya ce, Afirka ta kudu na alfahari da tawagar 'yan wasan ta, duba da yadda 'yan wasan suka sake nuna kwarewar su tsakanin sauran kasashen duniya. Kaza lika ya godewa daukacin al'ummar kasar bisa goyon baya da suka nunawa tawagar 'yan wasan.

Dan wasan tseren kasar Wayde van Niekerk ne ya fara lashe lambar zinari, bayan da ya karya matsayin bajimtar shekaru 17 da Michael Johnson ya kafa a gasar ta wannan karo.

Ita ma Caster Mokgadi Semenya, ta lashe lambar zinari ta gudun mita 800, bayan da ta kammala tseren ta cikin minti 1 da dakika 55.28, lambar da ta kasance ta 25, da Afirka ta kudun ta samu a tarihin gasar Olympic da ta halarta.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China