Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana yau Litinin cewa, a matsayin manzon musamman na shugaban kasar Sin, mataimakin shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Ma Biao, zai halarci bikin rantsar da mista Edgar Lungu a matsayin shugaban kasar Zambiya, bikin da za a gudanar a ranar 13 ga watan nan a birnin Lusaka, hedkwatar Zambiya. (Tasallah Yuan)