in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF na fatan za a kara yawan jari a fannin samar da abinci mai gina jiki a Afirka
2016-08-23 09:32:02 cri
Darakta mai kula da gabashi da kudancin Afirka ta asusun yara na MDD (UNICEF) Leila Gharagozloo-Pakkala ta yi kira ga masu ruwa da tsaki da su samar da karin hanyoyin bunkasa samar da abinci mai gina jiki, musamman ma ga kananan yaran dake yankunan kudu da hamadar Sahara.

Leila Gharagozloo-Pakkala, wadda ta yi wannan kira, yayin wani taron lalubo hanyoyin warware matsalar karancin abinci mai gina jiki tsakankanin kananan yara dake gudana a birnin Nairobin kasar Kenya, ta ce, duk da irin ci gaban da aka samu a shekarun baya bayan nan, akwai yara 'yan kasa da shekaru 5 da yawan su ya kai miliyan 55, wadanda ke fama da karancin abinci mai gina jiki a wannan shiyya.

Jami'ar ta kara da cewa, da dama daga rukunin wadannan yara na shafe kwanaki 1,000 na farkon rayuwar su ba tare da samun abincin mai nagarta ba. Mahalarta taron na wannan karo dai za su shafe kwanaki 4, suna nazartar hanyoyin dakile wannan matsala, sun kuma kunshi wakilai da masana daga kasashen Afirka a kalla 35.

Kafin kammalar taron, ana sa ran mahalartan sa za su duba yiwuwar kara zuba jari a fannin samar da abinci mai gina jiki ga yara ta hanyar hadin gwiwa da hukumomin cikin gida, da na sassa masu zaman kan su.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China