in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A yau ne, za a bude gasar Olympics a birnin Rio de Janeiro
2016-08-05 10:42:19 cri

A yau Jumma'a ne, za a bude gasar wasannin Olympics na yanayin zafi karo na 31 a birnin Rio de Janeiro dake kasar Brazil. Wannan shi ne karo na farko da za a yi gasar ta Olympics a nahiyar kudancin Amurka. Za a yi bikin bude gasar ne a filin wasan motsa jiki na Maracana.

Shugaban kwamitin shirya gasar wasannin Olympics na Rio Carlos Arthur Nuzman ya bayyana cewa, mun shirya sosai don kafa sabon tarihi. Kasar Brazil ta fuskanci matsaloli da dama a fannonin siyasa da tattalin arziki a lokacin da take shirye-shiryen daukar bakuncin gasar, amma duk da haka mun yi kokarin kammala ayyuka daban-daban, kuma za mu iya gudanar da wannan gasa cikin nasara.

Zakaran wasan takobi na maza a gasar Olympics ta London Lei Sheng, shi ne zai rike tutar tawagar kasar Sin a gasar mai mutane 711 da za ta halarci bikin bude gasar Olympics. 'Yan wasan kasar Sin 416 ne za su fafata a gasar, adadi mafi yawa a cikin tarihin gasar ta Olympics. Ana saran za su shiga manyan wasanni 26, da kuma kananan wsanni 210. Kamar kullum ana fatan, 'yan wasan kasar Sin za su yi kokarin lashe lambobin yabo na zinariya a wasannin kwallon tebur da wasan badminton da tsunduma cikin ruwa da wasan daga nauyi da kuma harbi.

A ranar 21 ga watan Agusta ne, ake fatan kammala gasar wasannin Olympics ta Rio.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China