Wadannan matsaloli dai sun haifar da damuwa ga jama'a, game da sha'anin kiwon lafiya yayin gudanar da gasar Olympics ta birnin Rio.
Bisa labarin da shafin Intanet na gasar wasannin Olympics ta Rio ya fitar, an ce, a kwanakin baya yayin da ministan kiwon lafiyar Brazil Ricardo Barros ke ganawa da jami'an kwamitin wasannin Olympics na duniya a birnin Geneva da ke kasar Switzerland, ya ce birnin Rio zai dauki likitoci 6,000 don ba da tabbaci game da sha'anin kiwon lafiya, don haka kwamitin wasannin Olympic na da kwarin gwiwa game da birnin ta fuskar kula da lafiya.(Bako)