in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira da a tsagaita bude wuta a duk fadin duniya a yayin gasar wasannin Olympics ta Rio
2016-07-30 12:42:57 cri
A jiya Jumma'a 29 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira da a tsagaita bude wuta a duk fadin duniya a yayin gasar wasannin Olympics ta Rio da na nakasassu.

Bisa al'ada, kamata ya yi bangarori daban daban su daina kowane irin yaki dake tsakaninsu daga kwanaki 7 kafin kaddamar da gasar wasannin Olympics na yanayin zafi a karo na 31 zuwa kwanaki 7 bayan gasar wasannin Olympics na nakasassu na yanayin zafi a karo na 15.

Ranar 29 ga wata, rana ce ta kwanaki 7 kafin kaddamar da gasar wasannin Olympics ta Rio, shi ya sa Ban Ki-moon ya yi kira da cewa, koda yake a daina tsagaita bude wuta sosai a duniya, amma tunanin Olympics na bukatar da a kawar da wahalhalu. Ya yi kira da a yi kokari kamar yadda ake neman samun lambobin yabo a yayin wasanni, domin cimma burin daina yake yake a duk fadin duniya a lokacin. Wannan zai bayyana ra'ayin gasar Olympics, wato girmamawa, da sada zumunci, da hadin kai, da kuma adalci.

Ban Ki-moon ya bayyana cewa, an kafa kungiyar 'yan wasa masu gudun hijira a wannan karo, hakan ya bayar musu zarafi na samun lambar kyauta. Wannan ya bayyana karfin 'yan gudun hijira, tare da bayyana wa duniya cewa, dole ne a kara kokarin daidaita matsalar 'yan gudun hijira, inda rikice-rikice suka zama dalilan wannan matsala. Shi ya sa bin tunanin Olympics na daina yake yake zai bayyana ra'ayin hadin kan kowa da kowa, in ji mista Ban.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China