in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar Laberiya ta kai ziyarar aiki a Nijar
2016-07-22 10:16:49 cri

Shugabar kasar Laberiya, kana kuma shugabar taron shugbannin kasashen kungiyar ECOWAS mai ci, madam Ellen Johnson Sirleaf, ta isa a birnin Niamey na kasar Nijar jiya Alhamis da safe, bisa tsarin wata ziyarar aiki da sada zumanta ta yini guda.

Shugabar Laberiya ta samu babban tarbo daga takwaranta na kasar Nijar Mahamadou Issoufou a filin saukar jiragen saman kasa da kasa na Diori Hamani, tare da sauran shugabannin hukumomin kasa, mambobin gwamnati, 'yan majalisu, da jakadun kasashen waje dake kasar.

Bisa jadawalin wannan ziyara ta yini guda a birnin Niamey, shugabannin biyu sun yi tattaunawa a fadar shugaban kasa, da kuma fadada tattaunawa tsakanin tawagogin kasashen biyu kan huldar dangantakar kasashen biyu da sauran batutuwan dake janyo hankalinsu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China