in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun dora muhimmanci sosai a kan yunkurin juyin mulkin kasar Turkiyya
2016-07-17 13:43:06 cri
Mukadashin babban hafsan-hafsoshin rundunar soja ta kasar Turkiyya Umit Dundar ya bayyana a jiya Asabar cewa, yunkurin juyin mulkin soja da aka yi a shekaran jiya a kasar Turkiyya ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 194, ciki har da 'yan sanda 41 da fararen hula 49 da wasu daga cikin wadanda suka shirya juyin mulkin 104. Kasashen Rasha da Pakistan da Girka da Somaliya da Jordan da kuma kungiyoyin EU da NATO sun dora mumuhimmanci sosai a kan wannan lamari.

Shugaban taron MDD na 70 Mogens Lykketoft, ya ba da sanarwa a jiya Asabar, inda ya yi Allah wadai da juyin mulkin da wasu sojojin kasar Turkiyya suka shirya.

Ban da haka kuma, shugaban kwamitin kungiyar EU Jean - Claude Juncker da shugaban kwamitin zartaswa na nahiyar Turai Donald Tusk da wakiliya mai kula da harkokin waje da tsaro ta kungiyar EU Frederica Mogherini sun ba da hadaddiyar sanarwa cewa, kasar Turkiyya muhimmiyar kawa ce ga kungiyar EU, kungiyar EU ta goyi bayan gwamnatin kasar da jama'a suka zaba. Kungiyar EU ta kuma yi kira ga kasar Turkiyya da ta farfado da tsarin kasar cikin gaggawa, kuma za ta ci gaba da zura ido kan yanayin kasar Turkiyyar tare da kasashe membobin kungiyar EU.

Wannan yunkurin juyin mulki ya kawo cikas ga huldar dake tsakanin kasar Turkiyya da Amurka. Gwamnatin Turkiyya ta zargi Fethullah Gulen, wani 'dan kasar Turkiyya dake gudun hijira a Amurka wajen kitsa wannan juyin mulki, ta kuma nemi gwamnatin kasar Amurka da ta tiso keyarsa zuwa gida. Dangane da lamarin, sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry, ya bayyana a jiya Asabar a birnin Luxembourg cewa, kasar Amurka za ta yi nazari kan wannan batu, amma ya kamata kasar Turkiyya ta shaida laifin Fethullah Gulen. Shugaban kasar Amurka Barack Obama ya nanata a jiya cewa, kasarsa za ta nace ga goyon bayan gwamnatin kasar Turkiyya, tana fatan kasar Turkiyya za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da ita domin tinkarar kalubale tare.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China