Mutane goma sha daya suka mutu, kana wasu hudu suka samu rauni mai tsanani a yayin wani harin kunar bakin wake da ya faru a cikin daren ranar Laraba zuwa Alhamis a Limani, birnin dake yankin kuriyar arewacin kasar Kamaru mai iyaka da Najeriya, a cewar wata hukumar yankin a ranar Alhamis da yamma ta kafar gidan rediyon gwamnati (CRTV).
Harin ya abku a ranar Laraba da misalin karfe tara da rabi na dare bisa agogon wurin kan wani dakin kallon bidiyo dake janyo gungun matasa 'yan lokuta kadan bayan an bude baki na watan Azumi, in ji gwamnan yaniin, Midjiyawa Bakari. (Maman Ada)