in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saurin bunkasuwar tattalin arziki na kungiyar ECCAS zai ci gaba da raguwa
2016-03-29 13:19:20 cri
Bisa labarin da jaridar Cameroon Tribune ta bayar, an ce, kwanan baya, kwamintin tsara manufofin kudi na bankunan kasashen da ke yankin tsakiyar Afrika ya shirya taro na shekarar 2016, inda suka bayyana cewa, tattalin arziki na kungiyar hadin gwiwa kan tattalin arziki na kasashen da ke yankin tsakiyar Afrika wato ECCAS zai ci gaba da tafiyar hawainiya.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a shekarar 2015, matsakaicin saurin bunkasuwar tattalin arziki na mambobin kasashe 6 na kungiyar ECCAS ya kai kashi 2.8 cikin 100, yayin da wannan adadi na shekarar 2014 ya kai kashi 4.8 cikin 100, an samu raguwa sosai.

Babbar hujjar da aka samu game da raguwar saurin bunkasuwar tattalin arziki a yankin shi ne, sakamakon faduwar farashin mai a kasuwannin duniya daga watan Yuni na shekarar 2014, da matsalar tsaro da ke ci gaba da tsananta a wannan yanki. Bisa hasashen da kwamitin tsara manufofi ya yi, a shekarar 2016, matsakaicin karuwar tattalin arziki na mambobin kasashe na kungiyar zai ragu zuwa kashi 2 cikin 100.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China