in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar asusun IMF ta bukaci a daidaita ayyukan da ake yi tskanin Birtaniya da EU
2016-06-27 13:55:38 cri
Shugabar asusun ba da lamuni na duniya IMF Madam Christine Lagarde ta bukaci kasar Birtaniya da kunigyar tarayyar kasashen Turai EU da su daidaita ayyukan da suke yi cikin sauri, don sassauta yanayin rashin tabbas da ficewar Birtaniya daga EU za ta haddasa.

Madam Lagarde ta bayyana haka ne a wani bikin nuna sabbin fasahohi da ya gudana a jihar Colorado ta kasar Amurka a jiya Lahadi, inda ta ce matakan da jami'an kasar Birtaniya da na kungiyar EU za su dauka a kwanaki masu zuwa za su tabbatar da yanayin da za a fuskanta a duk duniya. Don haka, a cewarta, asusun IMF ya sake bukatar bangarorin da abun ya shafa da su dauki matakan da suka dace wadanda za a iya hasashensu, don sassauta yanayin rashin tabbas, da tabbatar da gudanar aikin cikin zaman lafiya.

A cewar shugabar asusun IMF, da ma kasuwannin hada-hadar kudi ba su zaci cewa za a shiga wani babban yanayi mai hadarin gaske ba sakamakon ballewar Birtaniya daga kungiyar kasashen Turai, amma bayan da aka sanar da sakamakon zaben raba gardama a kasar Birtaniya matakin ya tayar da zaune-tashi a kasuwannin hada-hadar kudi na kasashe daban daban, har ma darajar musayar kudin Fam na kasar Birtaniya ta ragu da kimanin kashin 10%. Duk da haka, bai girgiza kasuwannin hada-hadar kudi ba, kana manyan bankunan kasashe daban daban sun shirya don kara samar da kudaden da ake bukata a kasuwanni.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China