in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF ya fara aiwatar da gyare-gyare kan kasonsa
2016-01-28 20:16:16 cri

Asusun ba da lamuni na IMF, ya fara aiwatar da gyare-gyare kan kasonsa da tsarin gudanarwa da aka amince a shekarar 2010, manufofin da za su baiwa kasashe masu saurin samun bunkasuwar tattalin arziki karin damar fada aji, a harkokin bada basuka na kasa da kasa.

Wata sanarwa da asusun ya fitar a jiya Laraba, ta nuna cewa gyare-gyaren su ne irin su mafiya girma, da asusun ya gudanar a manufofin sa na gudanarwa, tun bayan kafuwar sa, kuma sun yi la'akari da muhimmancin da kasashe masu saurin bunkasa ke da shi a harkokin tattalin arzikin duniya.

Sanarwar ta ce kasar Sin tana matsayi na uku a jerin masu fada aji game da hannayen jarin asusun, inda take biye da Amurka da Japan, wadanda ke gaban ta a wannan fage.

Kaza lika kasashen India, da Brazil da Rasha, su ma na cikin goman farko a wannan jadawali na IMF.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China