in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnonin manyan bankunan Afrika za su gana kan batun shigar da kudin Yuan na kasar Sin tsarin IMF
2016-06-19 12:42:26 cri
A kalla gwamnonin manyan bankunan kasashen gabashi da kudancin Afrika 14 ne za su gudanar da taro a Tanzaniya a Litinin, 20 ga wata, domin tattauna wasu batutuwa game da tasirin shigar da kudin Yuan na kasar Sin cikin jerin kudaden da aka lamunce yin amfani da su a tsarin kudaden kungiyar lamini ta IMF.

Taken taron dai shi ne, makomar shigar da kudin Yuan na Sin a tsarin IMF a matsayin halaltaccen kudi a tsarin kudaden ba da lamani.

Kasar Sin ta kasance a matsayin babbar abokiyar huldar kasuwanci da zuba jari a fannin samar da ababan more rayuwa da iskar gas da albarkatun man fetur da kasashen Afrika.

A wata sanarwar da babban bankin kasar Tanzaniya ya fitar a jiya Asabar ta nuna cewa, taron zai kuma tabo batun tasiri da kuma rawar da manyan bankunan kasashen za su taka game da ci gaban kananan bankuna raya sana'o'i da hada hadar kudade a yankunan.

Sanarwa ta kara da cewar mahalarta taron za su hada da gwamnonin manyan bankuna da na kanana da kuma sauran hukumomin al'amuran kudi na kasashen gabashi da kudancin Afrika. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China