in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matsalar jin kai na shafar yara fiye da miliyan biyu a Chadi
2016-06-17 09:43:37 cri

Fiye da yara miliyan biyu suke butatar taimakon jin kai a shekarar 2016 a Chadi, kasar da kuma a lokaci guda take fama da matsalar abinci, hijirar al'ummomi, bukatun kiwon lafiya da kuma bala'u daga indallahi, in ji Gianluca Flamigni, wakilin kungiyar UNICEF a kasar.

Ya jaddada wajabcin mayar da hankali sosai kan kare da ci gaban yara da suka kwashe fiye da rabin al'ummar kasar Chadi.

Ranar yaran Afrika, da aka yi bikinta a wannan shekara bisa taken "Yake yake da rikice rikice a Afrika, kare 'yancin dukkan yara" ta kasance ranar da gamayyar kasa da kasa ta kirkiro domin tunawa da kisan kiyashi na yaran Soweto a kasar Afrika ta Kudu a yayin da suke neman 'yancin samun ilimi mai inganci. Tun daga lokacin, wannan rana ta zama muhimmin lokaci na yin kiraye kiraye domin kare 'yancin yara. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China