Yan majalisar dokokin kasar Chadi sun amince, a ranar Litinin da wani kudurin kara tsawaita dokar ta baci a yankin tafkin Chadi har ta tsawon watanni shida.
Yaki da kungiyar Boko Haram, yaki ne mai sarkakiya dake bukatar lokaci idan ana bukatar samun nasara, bisa ga haka, mun cimma dabararmu ta aiki da lokaci, in ji ministan tsaron jama'a da hijira na kasar Chadi, mista Ahmat Mahamat Bachir. (Maman Ada)