in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya bukaci Guinea-Bissau da ta warware rikicin kasar ta hanyar siyasa
2016-06-16 10:12:29 cri

Kwamitin mai wakilan kasashe 15 na MDD, ya bayyana damuwarsa game da tabarbarewar al'amurra na baya bayan nan a kasar ta Guinea-Bissau, tun bayan samun bayanai da kwamitin ya yi game da halin da ake ciki a kasar.

Joao Soares Da Gama, jakadan Guinea-Bissau a MDD, ya sanar da kwamitin tsaro na MDD cewar, kasarsa ta gurgunce sakamakon rikicin siyasar da ya daidaita kasar na dogon lokaci.

A watan da ya wuce, shugaban kasar Guinea-Bissau Jose Mario Vaz ya ayyana Baciro Dja a matsayin sabon firaiministan kasar, lamarin da ya haddasa zazzafar mahawara daga bangaren magoya bayan jam'iyyar PAIGC.

A cewar Soares Da Gama, rikicin siyasar da ya dabaibaye kasar ya yi matukar haifar da komada ga ci gaban tattalin arzikin kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China