in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron Sin ya gana da takwaransa na Cote d'Ivoire
2015-04-23 11:00:16 cri
Ministan tsaron kasar Sin Chang Wanquan, ya gana da takwaransa na kasar Cote d'Ivoire Paul Koffi Koffi a jiya Laraba a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar tasu, Mr. Chang ya ce tun bayan kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da kasar Cote d'Ivoire, sassan biyu ke ci gaba da raya alakarsu cikin kyakkyawan yanayi. Ya ce, rundunar sojojin Sin na dora muhimmanci sosai game da zumuncin da ke tsakaninsu da takwarorinsu na kasar Cote d'Ivoire, kana suna fatan ci gaba da kokari tare da Cote d'Ivoire, wajen inganta ziyarar manyan jami'an gwamnatocin kasashen biyu, da mu'amalar jama'a tsakanin kasashen biyu, da yalwata hakikanin hadin gwiwar sojojin kasashen biyu, don daukaka zumunci a tsakanin sojojinsu.

A nasa bangare, Mr. Koffi ya ce, Sin sahihiyar abokiyar hulda ce ga Cote d'Ivoire. Kuma rundunar sojojin kasar na fatan kyautata huldar dake tsakaninsu, gami da karfafa hadin gwiwarsu a fannonin horar da ma'aikata da dai sauransu.

Kafin ganawar tasu dai, sai da Mr. Chang ya shirya bikin maraba da ziyarar Koffi a kasar Sin, kana ya zagaya da shi don kallon faretin sojojin ruwa, da na kasa, da sama na kasar Sin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China