in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da taka rawar gani wajen daidaita batun Syria ta hanyar siyasa, a cewar Wang Yi
2016-05-16 20:49:13 cri

A yau Litinin ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi tare da takwaransa na kasar Faransa Jean-Marc Ayrault sun gana da manema labaru a nan birnin Beijing, bayan kammala shawarwari .

Wang Yi ya ce kasar Sin na dora muhimmanci matuka kan batun Syria, kuma tana nuna goyon bayan ta ga bangarori daban daban na kasar, da su rungumi kuduri mai lamba 2254 na kwamitin sulhun MDD game da batun Syria, yana mai fatan bangarorin da batun ya shafa, musamman ma kasashen Rasha da Amurka, za su kara taka rawar da ta dace wajen tabbatar da tsagaita bude wuta, da daidaita batun Syria ta hanyar siyasa.

Bugu da kari, Mr. Wang ya yi kira ga bangarori biyu na kasar Syria, da su gudanar da shawarwari kai tsaye kuma a kan lokaci, domin cimma daidaito kan yadda za a daidaita batun Syria ta hanyar siyasa.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China