in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya: Matsakaicin GDP na 'yan kasar Kenya ya ninka na Uganda sau biyu
2016-05-16 10:11:27 cri
Rahoton baya bayan nan da bankin duniya ya fitar game da mizanin raya kasa, ya nuna cewa, matsakaicin GDP da kowa ne dan kasar Kenya ke samu ya kai dalar Amurka dubu 1.29, wato ya kusan ninka na kasar Uganda sau 2 (dala 670), kuma ya fi na kasashen Tanzania (dala 920) da Rwanda (700).

Yanzu ana samun karuwar 'yan kasar Kenya dake zaune a birane, inda kashi 56 cikin dari na mazauna birane a kasar suna zaune a unguwannin matalauta, kashi 63 cikin dari na dukkan 'yan kasar suna samun ruwa mai tsabta, kana kananan yara 'yan kasa da shekaru 5 da ke mutuwa ya kai 49 cikin 1000, wanda ya wuce matsayin yankin Afirka baki daya na 45 cikin 1000. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China