in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya za ta fara nazarin makamshin nukiliya da za ta yi amfani da shi
2016-05-03 10:31:32 cri
Mahukuntan kasar Kenya sun fara nazarin nau'in makamashin nukiliya da kasar za ta yi amfani da shi domin gina tashar samar da wutar lantarki mai aiki da makamashin nukiliya.

Mai rikon mukamin darektan tsare-tsare na hukumar samar da wutar lantarki ta kasar Kenya (KNEB)Winnie Ndubai ne ya shaida hakan ga manema labarai. Yana mai cewa, makamashin nukiliya ita ce hanya mafi dacewa ta samar da wutar lantarki da za ta taimakawa kasar Kenya wajen bunkasa harkokinta na tattalin arziki, don haka wajibi ne tsarin ya dace da yanayin kasar.

Hukumar samar da wutar lantarki ta kasar Kenya tana bukatar tashar samar da wutar lantarki da za a dogara da ita wajen samar da wutar lantarki nan da shekaru 20 masu zuwa.

A shekarar 2015 ne kasar Kenya ta bukaci hukumar kula da harkokin makashin nukiliya ta kasa da kasa (IAEA) da ta gudanar da bincike kan shirinta na raya makashin nukiliya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China