in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kenya ya ja hankalin kasashen Afirka game da batun hadin kai
2016-05-09 11:05:25 cri
Shugaba Uhuru Kenyatta na kasar Kenya, ya yi kira ga shugabannin nahiyar Afirka, da su ci gaba da aiwatar da manufofin da za su inganta hadin kan nahiyar.

Shugaba Kenyatta wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da fadar sa ta fitar a birnin Nairobi, bayan ganawar sa da ministan harkokin wajen kasar Equatorial Guinea Agapito Mba Mokuy, ya ce akwai bukatar kafa wata cibiyar nahiya, wadda za ta rika baiwa shuwagabannin Afirka horo game da dabarun bunkasa hadin kan kasashen nahiyar.

Ya ce kasar sa ta ci gajiyar irin wannan hadin kai, don haka take fatan daukar nauyin wannan cibiya, wadda za ta iya habaka harkokin siyasa da mulki a nahiyar.

Shugaban na Kenya ya kara da cewa, abun bakin ciki ne ganin yadda wasu daga masu tallafawa nahiyar ta Afirka ke amfani da dogaron da nahiyar ke yi kan irin wannan tallafi, wajen cimma muradun kashin kai, maimakon muradun al'ummar nahiyar.

Mr. Mokuy dai ya ziyarci birnin Nairobi ne a ranar Lahadi, domin isar da sakon musamman na shugaban Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema Mbasogo. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China