Haka kuma, sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi ta yi a birnin Nairobi, wani gini mai bene shida dake yankin Huruma a gabashin birnin Nairobi ya rushe a ran 29 ga watan Afrilu, lamarin da ya haddasa rasuwa da jikkatar mutane da dama, ban da haka kuma, ana ci gaba da samun wasu hadarurruka a sauran yankunan dake birnin Nairobi sakamakon wannan bala'i.
Kana, bisa labarin da aka samu, an ce, hukumomin da abin ya shafa na kasar Kenya sun riga sun rushe wasu gidajen da mai iyuwa ne za su yi rushewa ba zato ba tsammani sakamakon bala'in, domin kawar da sake faruwar iri wannan hadari. (Maryam)