in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta kawo goyon bayanta ga kasashen Afrika dake yaki da fataucin hauren giwa
2016-05-03 10:35:58 cri
Bayan kasar Kenya ta lalata a makon da ya gabata dukkan ajiyar hauren giwa da kahon bauna na kasar domin yin allawadai da farautar namun daji ba bisa doka ba, wasu manyan jami'an MDD sun kawo goyon bayansu ga kasashen Afrika dake yaki da kasuwancin nau'o'in namun daji ba bisa doka ba, a cewar wata sanarwa ta MDD.

A yayin wani bikin konawa da ya gudana a ranar Asabar a Nairobi, babban birnin Kenya, kusan ton 105 na hauren giwa da ton 1.3 na kahon bauna aka kona domin yin kira ga duniya da ta kawo karshen kasuwanci na hauruna da kahonnin nau'o'in namun daji, lamarin da ke taimakawa wajen kawar da wadannan dabbobi daga doron duniya.

Bikin da aka shirya bisa jagorancin Kenya Wildlife Service, wata hukumar gwamnatin kasar dake kula da kiyaye muhallin daji, wannan biki ya gudana a gaban idon shugabannin kasashen Kenya, Gabon da Uganda, da kuma mataimakin daraktan zartaswa na tsarin kula da muhalli na MDD (PNUE), mista Ibrahim Thiaw, da kuma shugabar tsarin ci gaba na MDD (PNUD), madam Helen Clark.

Ba za mu rufe ido ba a ci gaba da farautar namun daji ba bisa doka ba har karin rana daya ba, in ji mista Thiaw a cikin wata sanarwa a wannan rana, tare da kara cewa, wannan ya sabawa duk wani tunani, tattalin arziki da siyasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China