in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Somaliya da na AU sun sake kwace kauyen Runir daga hannun mayakan Al-Shabaab
2016-05-03 09:59:11 cri
Dakarun gwamnatin Somaliya da na kungiyar tarayyar Afirka ta AU da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya AMISON a takaice sun sake kwato kauyen Runir-good da ke yankin tsakiyar Shabelle a kudancin kasar Somaliya kwana guda bayan fadawar kauyen hannun mayakan Al-Shabaab.

Wani jami'in soja mai suna Abdullahi Macalli ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua ta wayar tarho cewa, dakarun hadin gwiwar ba su samu wata matsala wajen sake kwato kauyen ba. Ko da yake mahukuntan Somaliya sun bayyana cewa, an halaka sojojinsu guda 8 bayan da aka yi musu kwanton bauna, yayin da aka halaka mayakan Al-Shabaab 12.

Kwato kauyen na Runir-good ya kara adadin yawan kauyukan dake karkashin ikon gwamnati, sakamakon hare-haren hadin gwiwa da dakarun sassan biyu suka kaddamar.

A ranar Lahadi ne mayakan na Al-Shabaab suka sake kwato kauyen Runir-good, inda suka yi ikirarin halaka sojoji sama da 32, ciki har da wani babban jami'in soja a garin, kwana guda bayan da garin ya fada hannun sojoji gwamnati. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China