in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Somaliya da AU sun karbi yankuna da dama dake tsakiyar kasar daga hannun Al-Shabaab
2016-05-01 11:55:36 cri
Rundunar sojojin kasar Somaliya (SCN), tare da taimakon dakarun tawagar kungiyar tarayyar Afrika dake Somaliya (AMISOM), sun karbe a ranar Asabar ikon yankuna da dama dake yankin Moyen-Shebelle dake tsakiyar kasar Somliya, daga hannun kungiyar ta'addanci ta Al-Shabaab, in ji hukumomin wurin.

Kakakin hukumar yankin Middle Shebelle, mista Da'ud Haji Iro, ya bayyana cewa dakarun hadin gwiwa sun karbi ikon yankunan Runir-Dieu, Nur-Dugle, Ad-Adeyles dake yankin Moyen-Shebelle, bayan samame kan mayakan Al-Shabaab a safiyar ranar Abasar.

Dakarun SCN da AMISOM sun gudanar cikin hadin gwiwa wani samame kan kungiyar ta'addancin dake wannan yankin, kuma dukkan yankunan da aka karba daga hannun mayakan Al-Shabaab suna cikin kwanciyar hankali yanzu, in ji mista Iro.

An samu tirjiya daga wannan kungiya a yayin samamen, amma ba a samu asarar rayuka ba. Dakarun hadin gwiwa za su kwato bada jimawa ba sauran yankin daga hannun mayakan Al-Shabaab, in ji jami'in.

AMISOM ta fara jibge sojojinta a kasar Somaliya a shekarar 2007, dake kunshe da sojojin Kenya, Habasha, Uganda da Burundi. Tare da taimakonta, rundunar sojojin Somaliya sun samu nasara sosai kan Al-Shabaab da ta mamaye babban yankin tsakiyar Somaliya da na arewaci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China