in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hana zanga zangar maido da tsarin demokaradiyya a Nijar
2016-04-26 10:22:22 cri

Wata zanga zangar da ya kamata ta gudana a ranar Lahadi bisa jagorancin wasu kungiyoyin fararen hula na kasar Nijar ashirin a karkashin "gungun jan damara domin kare kasa" a dukkan fadin kasar, domin maido da tsarin demokaradiyya, hukumomin kasar sun hana ta bisa wasu dalilai na tsaro.

Makasudin wannan zanga zanga, a cewar masu shiryawa shi ne na yin allawadai da kura kuren da aka samu a lokacin zabukan baya bayan nan a kasar Nijar, wadanda suke sake baiwa shugaba mai ci Mahamadou Issoufou sake lashe zaben shugaban kasa, da kuma hana mulkin danniya a cikin wannan kasa dake yammacin Afrika, a cewarsu.

A birnin Niamey, ana sanar wa kungiyoyin fararen hula duk matakin hana zanga zangar a jajibiri, kuma an jibge jami'an tsaro a muhimman wurare tun safiyar ranar Lahadi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China