Jam'iyyun 'yan adawa 23 a janhuriyar Nijar, sun bayyana aniyar marawa Hama Amadou baya, a yayin zagaye na biyu na babban zaben kasar dake tafe.
Wata sanarwa da gungun jam'iyyun adawar suka fitar a birnin Yamai, ta ce jam'iyyun sun amince su aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla tun kafin zagayen farko na zaben, game da marawa duk wanda ya zo na biyu a zagayen farko na zaben baya.
Shi dai Hama Amadou ya kasance na biyu ne a zaben da ya gabata da kaso 17.7 bisa dari na daukacin kuri'un da aka kada, inda yake biye da shugaban kasar mai ci Mahamadou Issoufou, wanda ya samu kaso 48.4 bisa dari na jimillar kuri'un.(Saminu)