in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya jaddada bukatar daukar matakai don bullo da tsarin yaki da talauci na dogon lokaci
2016-04-25 13:36:13 cri
A jiya ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara lardin Anhui, inda ya isa garin Jinzhai na birnin Liu'an dake lardin Anhui, sannan ya tattauna tare da jami'ai da jama'a kan yadda za a yaki da talauci.

Garin Jinzhai yana yankin Dabie mai cike da tsaunuka, wannan ya sa ake kira sa da sunan wurin da aka kirkiro sojojin Red Army da hafsoshin soja, kana shi ne gari mafi fama da talauci a kasar Sin, ya zuwa karshen shekarar 2015, akwai matalauta fiye da dubu 80 a garin.

A wannan rana da yamma, shugaba Xi Jinping ya kai ziyara kauyen Dawan dake garin Jinzhai. Xi Jinping ya bayyana cewa, ba za a manta duk wani yanki ba yayin da ake kokarin cimma burin zaman wadata, musamman tsohon yankin kasar.

A lokacin yaki da 'yantar da jama'a ko a lokacin bude kofa da yin kwaskwarima, jama'ar yankin sun bayar da gudummawa sosai ga kasar. Kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya dora muhimmanci sosai kan aikin yaki da talauci a yankuna masu fama da talauci, don haka kamata ya yi a dauki matakai tare da bullo da tsarin yaki da talauci na dogon loakci don aiwatar da aikin a dogon lokaci da tabbatar da cimma burin zaman wadata a dukkan fannoni kafin shekarar 2020. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China