in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon zababben shugaban CAR zai hada kai da Sin
2016-03-21 09:37:20 cri

Sabon zababben shugaban kasar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya CAR Faustin Archange Touadera, ya yi alkawari karfafa hadin gwiwa da kasar Sin a matsayin babbar aminiyar ga kasar.

Touadera, ya fadi hakan ne a yayin zantawa da kamfanin dillancin labarum kasar Sin Xinhua a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce, CAR tana bukatar yin aiki tare da kasar Sin, domin kulla abokantaka da karfafa hadin kai a tsakanin kasashen biyu.

Touadera ya ce, akwai matukar bukatar farfado da ci gaban kasar cikin gaggawa, bayan shafe shekaru uku tana fuskantar yakin basasa, ya kara da cewar, sabuwar gwamnatin kasar, za ta ba da fifito ne wajen samar da tsaro, da zaman lafiya, da samun maslaha, da kuma hana yaduwar makamai a tsakanin jama'a.

Touadera ya jaddada muhimmancin farfado da tattalin arzikin kasar, yana mai cewa, CAR tana bukatar taimakon kasashen duniya domin dawo da yanayin tattalin arzikin kasar cikin hayyacinsa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China