in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco za ta janye dakarunta da ke aikin wanzar da zaman lafiya na MDD
2016-03-17 13:14:48 cri
Kasar Morocco ta bayyana aniyarta ta janyewa daga shirin kada kuri'ar raba gardama kan yankin yammacin Sahara(MINURSO) tare da janye dakarunta cikin tawagogin MDD guda uku da ke aikin wanzar da zaman lafiya, sakamakon kalaman baya-bayan da babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi game da yankin yammacin Sahara.

Kakakin MDD Stephan Dujarric wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai, ya bayyana cewa, tuni ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Morocco ta sanar da sakatariyar MDD game da matakin da kasar ke shirin dauka, wanda ya hada da rage wakilcinta a shirin na kada kuri'ar raba gardama game da makomar yankin, musamman reshen harkokin siyasa,da kuma kawo karshen irin gudummar da take bayarwa na sama da dala miliyan 3.

A kwanakin baya ne dai Ban Ki-moon ya ziyarci sansanonin 'yan gudun hijira da ke yammacin Sahara, inda ya kwatanta yankin a matsayin wanda aka mamaye shi. Wannan kalami ya haifar da zanga-zanga a Rabat abin da ya sanya gwamnatin Moroccon daukar wannan mataki.

Sai dai kakakin na MDD ya ce, Ban Ki-moon ba zai canja kalaman nasa ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China