in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kerry zai tafi Rasha don tattaunawa da Putin kan batun Syria
2016-03-16 10:02:36 cri

Sakataren harkokin kasashen wajen Amurka John Kerry a Talatan nan ya ce, zai tafi kasar Rasha makon gobe domin ganawa da shugaban kasar Vladimir Putin a kan batun rikicin Syriya.

Kafin ganawar sa da ministan harkokin wajen Georgia, Mikheil Janelidze, Mr Kerry ya ce, a lokacin ziyarar tasa a makon gobe bayan ganawa da shugaban kasar, zai kuma gana da ministan harkokin wajen kasar Sergey Lavrov domin tattauna yadda za'a matso da shirin siyasar kasar cikin sauri, sa'an nan kuma a yi kokarin amfani da wannan dama.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen na Amurka John Kirby ya ce, ranar da Mr Kerry zai kai ziyarar za ta kasance bayan Talatar makon gobe, lokacin da zai dawo daga ziyarar aiki a kasar Cuba tare da shugaba Barrack Obama.

Mr Kerry dai da alamun zai tattauna har da batun yanayin da ake ciki a gabashin Ukraine, tare da aiwatar da yarjejeniyar Minsk a lokacin ziyarar ta shi a Moscow, a cewar sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen ya fitar.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China