in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Kim Jong Un ya ce kasar sa na daf da fara gwajin makaman nukiliya
2016-03-15 10:47:53 cri

Shugaban kasar Koriya ta Arewa Kim Jong Un, ya bayyana aniyar kasar sa ta gudanar da gwajin makaman Nukiliya, tare da makamai masu linzami kirar roka nan da dan lokaci mai zuwa.

Kamfanin dillancin labaran kasar KCNA ne ya rawaito shugaba Kim na bayyana hakan, yayin da yake duba aikin gwaji na tsara muhallin harba makami mai linzami na kasar.

An gudanar da aikin gwajin ne domin tantance sabbin fasahohin da kasar za ta yi amfani da su a nan gaba, domin tabbatar da nasarar harba makamai masu linzami.

KCNA ya ce, an cimma nasara a gwajin sabbin fasahohin da kasar ta aiwatar.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China