Gwamnatin Korea ta Arewa DPRK ta yi kira da a kawo karshen arangama tsakaninta da Korea ta Kudu, tare da kara dankon dangantaka tsakaninsu.
Wannan kiran na kunshe a cikin wata sanarwar gwamnati, wacce aka baiwa kamfanin dillancin labarai na kasar KCNA.
Korea ta Arewa ta gabatar da wadansu shawarwari guda hudu, wadanda suka fayyace manufofinta da alkiblar da ta dauka wajen dakusar da tashin hankali a tsibirin na Korea, tare da kaiwa ga nasarar hadewar arewaci da kudancin tsibirin, wato shekaru 20 bayan rasuwar tsohon jagoran kasar, Kim II Sung. (Suwaiba)