in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan mai a Najeriya sun fara zanga-zangar gama gari
2016-03-10 09:28:35 cri

Ma'aikatan mai a Najeriya sun kaddamar da zanga-zanagr gama gari a ranar Laraban nan, abin da ya dakatar da ayyukan matatar man kasar ta NNPC, bayan da gwamnati ta sanar da kasa kamfanin zuwa rukuni 7 a ranar Talatan makon nan.

Karamin ministan mai kuma shugaban kamfanin mai na kasar wato NNPC ya ce, an dauki wannan mataki ne bayan ganawa da manyan kamfanonin mai.

Sai dai kuma zanga zangar gama gari karkashin jagorancin kungiyar ma'aikatan ta NUPENG da kuma PENGASSAN sun bayyana fusatar su a kan hakan.

Kungiyoyin sun zargi gwamnati da kin jawo masu ruwa da tsaki a cikin shawarar da suka yanke, abin da ya sa suka bukaci a yi watsi da shi.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China