in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ba za ta tura dakarunta Najeriya don yakar Boko Haram ba
2016-03-10 09:08:46 cri

Rundunar tsaron Afrika ta kudu ta yi watsi da rade radin da ake bazawa, cewar, za ta aike da dakarunta zuwa Najeriya domin yaki da kungiyar Boko Haram.

Mai magana da yawun rundunar sojin kasar Afrika ta kudu Siphiwe Dhlamini, ya fada wa manema labarai cewar, kawo yanzu gwamnatin kasar ba ta zartar da wani kuduri ba na tura dakarunta don yakar kungiyar Boko Haram.

Jita jitar dai ta kunnu kai ne, tun lokacin da shugaba Jacob Zuma na Afrika ta kudun ya kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu zuwa Najeriya a wannan mako, domin tattaunawa game da tura dakarun tsaro na musamman don ci gaba da yakar kungiyar mai kaifin kishin Islama.

Wannan rade radin ya ci gaba da bazuwa ne, bayan da ministan tsaron Afrika ta kudu Nosiviwe Mapisa-Nqakula ya gana da takwaransa na Najeriyar Mansur Dan Ali a farkon wannan makon.

A sanarwar da aka fitar bayan tattaunawar su da shugaba Muhammad Buhari, Zuma ya bayyana cewar, ganawar tasu ta tabo batun yin hadin gwiwa a matakin shiyya, da ma nahiyar domin dakile ayyukan ta'addanci.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China