in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Somaliya ta kaddamar da wani sabon shiri na siyasar ketare bayan shekaru 20 na yakin basasa
2016-02-08 12:47:07 cri
Kasar Somaliya ta kaddamar a ranar Lahadi da wani sabon shiri na siyasar waje na baki daya domin jagorantar huldarta tare da kasashen duniya, kan muhimman batutuwa kamar kasuwanci da kuma yaki da ta'addanci. A cewar wata sanarwa ta ma'aikatar harkokin wajen Somaliya, kaddamar da sabon shiri na siyasar waje na daya daga cikin wani muradi mafi girma domin tabbatar da cewa kasar ta kasance wata mai taka muhimmiyar rawa a cikin harkokin kasa da kasa.

Siyasar waje ta kasar Somaliya an gina ta bisa muhimman ginshikai na bunkasa dorewar zaman lafiya da tsaro a cikin kasa, shiyya da kuma kasa da kasa tare da taimakon halartar gaba daya a cikin diplomasiyyar huldar dangantaka, a cewar wannan sanarwa ta ma'aikatar harkokin wajen Somaliya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China