Wannan sanarwa ta jaddada cewa, dole ne a yanke hukunci kan masu kai harin. Kuma ya nemi a dauki kwararan matakan toshe hanyoyin samun kudi na kungiyar Al Shabaab da sauran kungiyoyin ta'addanci.
Bugu da kari, wannan sanarwa ta sake bayyana cewa, kowane irin harin ta'addanci da ake kai ba zai girgiza niyyar kwamitin sulhu na MDD na kokarin shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar Somaliya ba, kwamitin yana fatan babban zaben da za a yi a kasar Somaliya zai taka rawa wajen dawo da zaman lafiya a kasar. (Sanusi Chen)