in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bai wa Angola kyautar kudi cikin gaggawa
2016-02-05 20:21:42 cri

Gwamnatin kasar Sin ta tsai da kudurin bai wa gwamnatin kasar Angola kyautar kudi na dalar Amurka dubu 500 cikin gaggawa, a kokarin taimakawa jama'ar kasar sayen allurar rigakafin zazzabin shawara domin yaki da cutar cikin hanzari.

Wakilinmu ya samu wannan labari ne yau Jumma'a 5 ga wata daga ma'aikatar harkokin kasuwanci ta kasar Sin.

An ba da labarin cewa, ya zuwa karshen shekarar bara ta 2015, zazzabin shawara ta kama wasu mutane tare da halaka wasu a birnin Viana da ke lardin Luanda na Angola. Da zummar hana yaduwar cutar, gwamnatin Angola ta roki kasar Sin ta ba da taimakon gaggawa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China