in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta goyi bayan Palastinawa da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya
2016-02-01 10:49:06 cri

Wakilin Sin na musamman kan al'amurran yankin Gabas ta Tsakiya Gong Xiaosheng, ya fada a Lahadin nan cewar, kasar Sin tana goyon bayan al'ummar Palasdinawa da kuma shirin samar da zaman lafiya a yankin.

Wakilin, ya furta hakan ne ga manema labaru a birnin Ramallah dake gabar yammacin kogin Jordan, yayin wata ziyara inda ya bayyaba cewar, bai kamata ba a mayar da al'ummar Palasdinawa tamkar saniyar ware, kuma kasar Sin tana goyon bayan kafa yantacciyar kasar Palastinu mai ikon cin gashin kanta.

A cewar mista Gong, ziyarar kwanan nan da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya kai a yankin Gabas ta Tsakiya, wasu alamu ne dake nuna sabuwar dangantaka tsakanin kasar Sin da Palastinu, dama sauran kasashen dake shiyyar.

Ziyarar wacce ita ce ta farko ta rangadin shugaban a shekarar 2016, kuma ita ce ziyararsa ta farko a yankin tun bayan darewarsa kujerar shugabancin kasar. A lokacin da shugaba Xi ke gabatar da jawabi a taron kasashen Larabawa a birnin Alkahira, babban sakon dake kunshe cikin jawabin nasa shi ne, batun aniyar kasar Sin na tabbatar da zaman lafiya, da kwanciyar hankali da kuma samun bunkasuwa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China