in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Mutane miliyan 14 a kudancin Africa na fuskantar barazanar yunwa a sanadiyyar fari
2016-01-19 10:45:50 cri
Mai Magana da yawun MDD ya fada a Litinin din nan cewar, shirin samar da abinci na duniya (WFP) yayi kiyasin mutane miliyan 14 ne suke fukantar barazanar matsalar yunwa a kasashen kudancin Afrika, sakamakon matsanancin fari, lamarin da ya haifar da rashin wadataccen abinci a daminar bara.

Mataimakin kakakin MDD Farhan Haq, ya shedawa manema labarau cewar WFP ya tabbatar da cewar, matsalar karuwar dumamar yanayi na El Nino shine ummul aba isin daya haddasa matsalar ta fari a yankunan, kuma tuni matsalar ta fara shafar kayan amfanin gona.

Acewar WFP, makatsalar zatafi kamari ne a kasashen Malawi, da Madagascar da kuma Zimbabwe. Tuni kasar Lesotho ta kaddamar da wani shirin daukin gaggawa game da matslar fari a watan daya gabata, kuma kusan kashi daya bisa uku na alummar kasar basu da wadataccen abinci.

Haq, yace sauran kasashe da matsalar ta shafa sune Angola, Mozambique, da da kuma Swaziland.

Ita dau matsalar ta El Nino, tana haifar da kamfar ruwan sama a fadin yankin na kudancin Afrika tun a shekarar bara, lamarin da ya haifar da bushewar amfanin gona. A baya dai Afrikan ta kudu na fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen ketare, amma a halin yanku tana bukatar shigo da kayan abinci kimanin tone miliyan 5 zuwa 6 na masara daga kasashen ketare a sakamakon wannan matsala.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China