in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Merkel ba za ta halarci taron dandalin Davos ba
2016-01-11 16:05:14 cri
Gwamnatin kasar Jamus ta bayyana cewa, shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ba za ta halarci taron dandalin tattaunawa na Davos da za a gudanar a kasar Switzerland ba, sakamkon cin zarafin wasu mata da aka yi a birnin Köln.

A daren ranar 31 ga watan Disamba na shekarar 2015 ne, aka sace tare da cin zarafin wasu mata a birnin Köln da ke kasar ta Jamus, lamarin da ya tayar da hankulan jama'a sosai a kasar Jamus.

Jamusawa sun shafe kwanaki a jere suna gudanar da zanga-zangar nuna rashin jin dadinsu kan wannan batu.

Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Jamus ta bayyana cewa, 'yan sandan kasar sun tabbatar da cewa, daga cikin mutanen da ake zarga da aikata laifin, har da 'yan gudun hijira fiye da 20 da wadanda suke neman mafaka. Ministan dokokin shari'a na kasar Jamus Heiko Maas ya jaddada a jiya cewa, ba za a iya tabbatar da cewa, ko dukkan 'yan gudun hijira suna bin dokoki ko a'a bisa wannan batu ba. Amma Maas ya yi nuni da cewa, batun cin zarafin mata a Köln batu ne da aka tsara shi, hukumomin shari'a na kasar Jamus suna gudanar da bincike don gano wadanda ke da hannu wajen tsara cin zarafin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China