in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AL ta zargi Iran da shiga harkokin cikin gidan kasashen Larabawa
2016-01-11 10:06:53 cri

Kungiyar hada kan kasashen Larabawa ko AL a takaice ta zargi kasar Iran da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasashen.

Shugaban kungiyar Nabil al-Arabi ne ya sanar da hakar yayin taron ministocin harkokin wajen kungiyar da ya gudana a kasar Masar don tattauna takaddamar siyasar da ta kunno kai tsakanin Saudiya da kasar Iran.

Nabil al-Arabi ya bukaci dukkan kasashen Larabawa da su dauki matsayi guda kan wannan takaddama. Sannan ya yi kira ga kasar Iran da ta daina tsamo baki a harkokin cikin gidan kasashen.

Taron kungiyar kasashen Larabawan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar mummunan zaman tankiya da barazanar tsaro a yankin gabas ta tsakiya.

Yanzu haka dai dukkan kasashen Larabawa sun bayyana cikakkiyar goyon bayan su ga kasar Saudiya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China