Hukumar shirya wasannin kwallon kafa ta Afrika CAF ta gudanar da bikin raba kyautuka ga fitattun yan wasan kwallon kafa na Afrika a Abuja, helkwatar mulkin Najeriya, bikin wanda aka gudanar a a jiya Alhamis da yammaci.
Wannan biki ya kasance wani gagarumin biki a harkar kwallon kafa da aka taba gudanarwa a nahiyar Afrika, kuma a lokacin bikin, shahararrun 'yan wasa maza da mata da masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa daga sassan dabam dabam sun halarci bikin. Wannan shi ne karo na 44 da hukumar ta CAF ta shirya irin wannan biki. Ahmad Fagam)